An rufe Jami’ar Kogi saboda zanga-zangar ɗalibai
Daliban sun tare babbar ƙofar shiga jami’ar ne tun bayan haɗarin da ya yi sanadin mutuwar ɗaliban jami’ar biyar.

Hukumomin Jami’ar Tarayya da ke Lokoja a Jihar Kogi, sun rufe jami’ar har zuwa wani lokaci domin daƙile ci gaba da asarar rayuka da dukiya.
Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun magatakarda kuma sakatariyar majalisar Jami’ar, Dokta Rebecca Aimiohu Okojie, a ranar Alhamis kuma ta bayyanawa manema labarai a Lokoja.
- Jihar Gombe na ƙarfafa haƙƙoƙin yara masu nakasa — Ƙungiyar JONAPWD
- NNPP ta rasa Ɗan Majalisa na farko da ya koma APC
Hukumar Jami’ar ta yi zargin cewa, ɗaliban sun tare babbar ƙofar shiga jami’ar ne tun bayan haɗarin da ya yi sanadin mutuwar ɗaliban jami’ar biyar a ranar Litinin, wanda ya sa shiga harabar jami’ar ke da wuya.
“Rufewar jami’ar ya biyo bayan asarar rayuka da ɗalibai biyar suka yi a wani mummunan haɗarin tirela a Felele, ranar Litinin 17 ga Fabrairu, 2025.
“Tun faruwar lamarin, ɗalibai sun tare ƙofar jami’ar duk da kakkausar murya daga gwamnatin jihar da kuma ƙoƙarin da hukumomin jami’ar suka yi na a kwantar da hankula.
“Saboda haka, bisa shawarar hukumomin tsaro na jihar da kuma daƙile ci gaba da asarar rayuka da dukiya, shugaban jami’ar bayan shawarwarin hukumar ta yanke, shawarar a madadin majalisar jami’ar cewa jami’ar, jami’ar da rassanta za a rufe su har sai baba-ta-gani. Ɗalibai za su bar wuraren karatu kafin ƙarfe 12 na rana ranar Alhamis, 20 ga Fabrairu.”