Ƙungiyar Ƙwadago ta tsunduma yajin aiki

Ƙungiyoyin Ƙwadagon sun zargi Gwamnatin Tarayya da gaza cika alkawarin da suka ƙulla a bara.

Ƙungiyar Ƙwadago ta tsunduma yajin aiki

Zanga-zangar NLC

Gamayyar Kungiyoyin Ƙwadago da suka haɗa da Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya NLC da Ƙungiyar ‘Yan Kasuwa ta Kasa (TUC) sun ayyana shiga yajin aikin kwanaki 14 kamar yadda suka sanar da Gwamnatin Tarayya.

Yajin aikin kamar yadda sanarwar ta bayyana zai fara ne daga gobe Juma’a, 9 ga watan Fabarairu.

’Yan Ƙwadagon dai sun zargi Gwamnatin Tarayya da gaza aiwatar da yarjejeniyar da suka ƙulla da ita tun a watan Oktoban bara.

‘Yarjejeniyar da gwamnatin Najeriya ta cimma da kungiyoyin kwadagon, ta kunshi inganta albashin ma’aikata, daidaita farashin man fetur da kuma shawo kan matsalar karyewar darajar kudin kasar wato Naira.

NLC da TUC sun ce, halin tsadar rayuwa da ‘yan Najeriya ke ciki abin dubawa ne matuka, amma sun ga alamun gwamnati ta yi biris da wannan matsala.

Hakan ta sanya ma’aikata a kasar suka yanke shawarar tafiya yajin aikin gargadi na tsawon makonni biyu, har zuwa lokacin da gwamnati za ta waiwaiyi ‘yan Najeriyar.

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan

A tabbatar an mutunta tsarin dimokuraɗiyya a Zaɓen Edo — Tinubu