Masu zanga-zanga da tutar Rasha sun fasa banki a Kaduna

Ɓata garin sun lalata motoci da dukiyoyin ma’aikatan bankin.

Masu zanga-zanga da tutar Rasha sun fasa banki a Kaduna

Wasu ɓata gari ɗauke da tutar ƙasar Rasha sun shiga cikin masu zanga-zangar yunwa, tare da fasa wani banki a Jihar Kaduna.

Zanga-zangar dai ta rikiɗe zuwa tashin hankali a rana ta biyar a jihar, inda wasu ɓata gari suka kai hari banki a yankin Tudun Wada na Kaduna.

Ɓata garin sun lalata motocin ma’aikatan bankin sannan suka sace kayayyakin kuɗi masu tarin yawa.

Gwamnan jihar, Uba Sani, ya sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a yankin Kaduna da Zariya, biyo bayan tashe-tashen hankula da aka samu.

Tun daga wannan lokaci, jami’an tsaro suka shiga tarwatsa ɓata garin da ke ƙoƙarin satar kayan mutane da kuma tabbatar da zaman lafiya a jihar.

A ranar Alhamis ne, aka kama aƙalla mutum 25 da suka fasa shagunan mutane tare da sace musu kayayyaki a ranar farko ta zanga-zangar yunwa a jihar.

Zanga-zangar ta rikiɗe zuwa tashin hankali a yankin Kaduna ta Arewa da wasu sassan Kaduna ta Tsakiya, yayin da yankin Kaduna ta Kudu ke cikin kwanciyar hankali.

Tuni tituna a Jihar Kaduna, sun zama fayau babu mutane tun bayan saka dokar hana fita.

Mazauna Kaduna sun yaba wa gwamnan jihar bisa saka dokar.

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan