Ɗan sanda ya rataye kansa har lahira a Neja

Kakakin rundunar ya ce har yanzu ba a gano dalilin da ya sa jami’in ya rataye kansa ba.

Ɗan sanda ya rataye kansa har lahira a Neja

Wani Mataimakin Sufeton ’Yan Sanda (ASP), Shafi’u Bawa, da ke aiki da Rundunar 61 Police Mobile Force a Kontagora da ke Jihar Neja, ya hallaka kansa har lahira.

Wani jami’in dan sanda ya shaida wa Aminiya cewa, lamarin ya faru ne a ranar Asabar.

An tsinci gawarsa rataye a cikin dakinsa.

Majiyoyi sun ce mahaifinsa, Malam Usman Bawa ne, ya fara gano abin da ya faru sannan ya kai rahoton lamarin zuwa ofishin ’yan sanda da ke Kontagora.

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce: “A ranar 8 ga watan Fabrairu, 2025, da misalin karfe 2 na rana, an samu rahoton cewa ASP Shafi’u Bawa na Rundunar 61 PMF, Kontagora, ya rataye kansa.

“Har yanzu ba a san dalilin da ya sa ya aikata hakan ba.

“An dauke gawarsa tare da mika ta ga iyalansa domin yi mata jana’iza.

“Ana ci gaba da bincike don gano musabbabin faruwar lamarin.”

Gwamna Sule ya naɗa Kwamishinoni 16 a Nasarawa

Atiku da Obasanjo suna ganawar sirri

Ɗalibi ya kashe abokin karatunsu da gatari a Nasarawa

Sojoji sun tarwatsa maɓoyar Bello Turji a Zamfara