2023: Ina da yakinin za a yi sahihin zabe —Jega
Jega ya ce yana da yakinin Najeriya za ta gudanar da sahihin zabe a 2023 duk da kalubalen da take fuskanta.
Tsohon Shugaban Hukumar INEC, Farfesa Attahiru Jega
Tsohon shugaban Hukumar Zabe ta Kasa(INEC), Farfesa Atahiru Jega, ya ce yana da yakinin Najeriya za ta gudanar da sahihin zabe a 2023 duk da kalubalen da take fuskanta.
Jega ya bayyana hakan ne a wajen taron karrama Farfesa Adele Jinadu da aka gudanar a Abuja.
- NAJERIYA A YAU: Matsayin Kuri’ar ’Yan Gudun Hijira A Zaben 2023
- Samun man fetur a Arewa babbar nasara ce
Ya ce, duk da hare-haren da ake kai wa cibiyoyin INEC da kuma tashin-tashinar yakin neman zaben da ake gani, yana da tabbacin hakan ba zai hana gudanar da ingantaccen zabe ba a badi.
Ya kara da cewa, duk da dai yana ji wa sakamakon zaben tsoro, amma yana da yakinin a kan makomar kasar.
Haka nan, ya ce duk da abubuwa marasa dadi da wasu shugabannin siyasa ke jagorancin aikatawa, yana fatan tsabtataccen zabe zai samu a kasar a 2023.
(NAN)