2027: Kotu ta ayyana ranar yanke hukunci a shari’ar neman cancantar takarar Jonathan
Cikin ƙarar da aka shigara ana neman kotu ta hana Jonathan tsayawa takarar shugaban ƙasa a Zaɓen 2027 a kowacce jam’iyya.
Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja, ta ayyana 26 ga watan Mayun bana a matsayin ranar da za ta yanke hukunci a ƙarar da ke neman cancantar tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, ta tsayawa takarar shugaban ƙasa a Zaɓen 2027.’
Mai shari’a Peter Lifu ne ya ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar yanke hukunci bayan sauraron hujjojin lauyoyin mai ƙara da kuma waɗanda ake ƙara.
- APC ta tabbatar da nasarar Yusuf Gadgi a Mazabar PKK
- ’Yan ta’adda sun kashe mutum 10 a kasuwa a Katsina
Aminiya ta ruwaito cewa, wani mutum mai suna Jideobi ne ya shigar da ƙarar yana neman kotu ta hana Jonathan tsayawa takarar shugaban ƙasa a Zaɓen 2027 a ƙarƙashin kowacce jam’iyya.
Mai ƙarar ya kuma roƙi kotun da ta hana Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC karɓa ko tantance sunan Jonathan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa.
A ƙunshin ƙarar da ya shigar, ya nemi kotun da ta warware tufkar da ke cikin tanade-tanaden sashe na 1(1), (2), (3) da kuma 137(3) na Kundin Tsarin Mulkin 1999, wadda ka iya halasta ko haramta wa Jonathan cancantar sake neman kujerar shugaban ƙasa.