A tallafa wa gwamnatin Buhari da addu’a – dan Hadeja
Shugaban kungiyar masu Kishin Jam’iyyar APC (Patriotic Forum), reshen Arewa maso Yamma, Alhaji Umar dan Hadeja, ya roki al’ummar kasar nan su dage da addu’ar neman samun nasara ga gwamantin Shugaba Muhammadu Buhari, ta yadda za a cimma nasara shawo kan matsalolin da suka addabi kasar nan da suka hada da tsaro da tattalin arziki.Alhaji […]
Shugaban kungiyar masu Kishin Jam’iyyar APC (Patriotic Forum), reshen Arewa maso Yamma, Alhaji Umar dan Hadeja, ya roki al’ummar kasar nan su dage da addu’ar neman samun nasara ga gwamantin Shugaba Muhammadu Buhari, ta yadda za a cimma nasara shawo kan matsalolin da suka addabi kasar nan da suka hada da tsaro da tattalin arziki.
Alhaji Isyaku Umar dan Hadeja, ya bayyana haka ne a wajen taron kungiyar na yankin Arewa maso Yamma, da aka gudanar a otel din Criss Cross da ke Kano.
Umar dan Hadeja, ya nanata bukatar da ke akwai ta ’yan Najeriya su taimaka wa kansu da gwamnati mai mulki wajen shawo kan matsalolin tsaro da cin hanci da rashawa.
“Duk da cewa muna murna da samun managarcin Shugaban kasa Muhammadu Buhari, dole ne mu yi kira ga daukacin al’umma su ci gaba da addu’ar samun nasara ga gwamnatinsa, su kuma kara hakuri, tare da tallafa wa gwamnati wajen yaki da rashin tsaro da cin hanci da rashawa, mwadanda su ne matsalolin da suka yi wa kasar nan katutu, suka dakile ci gabanta,” inji shi.
A wurin taron, jiga-jigan kungiyar da suka hada Balarabe Wakili da Ibrahim Harisu da Abubakar Ahmed Dogo Mai Rumbun Iska, sun ce kungiyar za ta himmatu ka’in-da-na’in wajen fadakar da al’ummar kasar nan kan da tsare-tsare gwamnatin Buhari, ta yadda kowa zai bayar da