Abba ya nada Sheikh Daurawa shugabancin hukumar Hisbah ta Kano

A baya dama ya taba rike hukumar har sau biyu

Abba ya nada Sheikh Daurawa shugabancin hukumar Hisbah ta Kano

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya nada malamin addinin Musuluncin nan, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa shugabancin Hukumar Hisbah ta Jihar.

A baya dai, Sheikh Daurawa ya taba jagorantar hukumar har sau biyu, a zamanin mulkin tsohon Gwamnan Jihar, Rabi’u Musa Kwankwaso da kuma farkon mulkin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje.

Sai dai a shekara ta 2018, Daurawa ya sanar da ajiye mukamin lokacin da aka samu sabani tsakanin Kwankwaso da Ganduje.

Amma a ranar Litinin, malamin ya wallafa wani bidiyo da ya nuna shi yana karbar takardar sake nada shi shugabancin hukumar a karo na uku, daga Sakataren Gwamnatin Jihar, Dokta Baffa Abdullahi Bichi.

Ana ganin malamin ya taka muhimmiyar rawa wajen samun nasarar gwamnatin Jihar mai ci ta jam’iyyar NNPP.

Kotu ta tsige Ohinoyi na Ƙasar Ebira

Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Kano

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Noma Ba Tare Da Kashe Kuɗi Da Yawa Ba

HOTUNA: Hatsarin tirela ya yi ajalin mutum 4, shanu 15 da awaki 20 a Neja