Alhaji Adamu Falke ya kwanta dama

Allah ya yi wa Alhaji Adamu Falke, wanda aka fi sani da Alhaji Ada Falke rasuwa yana da shekaru 58 a duniya. Marigayi Alhaji Adamu ya rasu ranar Alhamis da ta gabata a Jihar Kano bayan gajeruwar rashin lafiya.Alhaji Adamu kani ne ga dillalin jaridar Aminiya a filin saukar jiragen sama na Murtala Muhammed da […]

Alhaji Adamu Falke ya kwanta dama
Alhaji Adamu Falke ya kwanta dama

Allah ya yi wa Alhaji Adamu Falke, wanda aka fi sani da Alhaji Ada Falke rasuwa yana da shekaru 58 a duniya.

Marigayi Alhaji Adamu ya rasu ranar Alhamis da ta gabata a Jihar Kano bayan gajeruwar rashin lafiya.
Alhaji Adamu kani ne ga dillalin jaridar Aminiya a filin saukar jiragen sama na Murtala Muhammed da ke yankin Ikeja a Jihar Legas, Alhaji dallami Ibrahim.
Ya mutu ya bar matarsa ta aure da ’ya’ya bakwai, wadanda suka hada da Alhasan da Muhammdu da Aminu-Alajeje da Zahara’u da Maryam da Humaira da kuma Bilkisu.
Alhaji Adamu ya bar aikin gwamnati a mukamin darakta a ma’aikatar ilimi ta Jihar Kano.
kanensa Alhaji danlami, dillalin jaridar Aminiya a Jihar Legas ya bayyana shi a matsayin mutum mai hakuri.
Tuni aka yi jana’izarsa a safiyar ranar Juma’ar da ta gabata.
Manyan malamai da ’yan kasuwa da kuma ma’aikatan Gwamnatin Jihar Kano ne suka halarci jana’arsa.