Allah Ka ba mu zaman lafiya

Ta’ala kadiri Ka ban lafiya In rera waken zaman lafiya.  Ka ba ni hazaka har da fasaha Gurin rera wakar zaman lafiya.  Tsira aminci su tabbata gun Muhammadu Manzon zaman lafiya. Ba shi kadai ba har da sahabbai Da alu da matansa baki daya. Ya bar wasiyya ga umma tasa Su zanka shiri don zaman […]

Allah Ka ba mu zaman lafiya


Ta’ala kadiri Ka ban lafiya

In rera waken zaman lafiya.


 Ka ba ni hazaka har da fasaha

Gurin rera wakar zaman lafiya.


 Tsira aminci su tabbata gun

Muhammadu Manzon zaman lafiya.


Ba shi kadai ba har da sahabbai

Da alu da matansa baki daya.


Ya bar wasiyya ga umma tasa

Su zanka shiri don zaman lafiya.


Ya zo da sako na jalla gare mu

Islam nufinsa zaman lafiya.


Jigo biyar ne inji Muhamman

Biyo ni ka ji su ga baki daya.


Farkonsu Kalmar Shahada ka gane

Biyayya ga Allah zaman lafiya.


Yarda da sakon Muhammadu shi ma

Yana kai ga turbar zaman lafiya.


Na biyyunsu Sallah na khamsu biyar ne

Da ba su yuwa sai akwai lafiya.


Ga Ramalana mu zan azuminsa

Kaza ba da Zakka zaman lafiya.


Cikon nasu Hajji ka je in da hali

Guzuri da hanyarka mai lafiya.


Sahabi ya ce ya Rasulu gaya min

Zan sam sawaba zaman lafiya?


In na rike su biyar babu kari?

Manzo ya ce har ka zam lafiya.


A gobe kiyama a saka a Jannah

Nan ne tukewar zaman lafiya.


 Ta yaya Musulmi a yau sunka baude

Wa horo na Manzon zaman lafiya?


Su kafirta bayi da Kalmar Shahada

Suna rushe sakon zaman lafiya.


Wasunsu gama har makamai gare su

Gilla suke ba zaman lafiya.


A Yerwa da Bama da Baga da Gwoza

Banki, Chibok ba zaman lafiya.


Sukan harbe mata da yara da tsofi

Samari su sace su baki daya.


Sukan sace mata da ba su da aure

Su auresu karhan suna fariya.


Su je makaranta su kona ta kurmus

Da yara cikinta ga baki daya.


Su ce musu arna da Kalmar Shahada

A baki, su fille su ba yafiya.


Boko Haramunga sun mana illa

Sun ci amanar zaman lafiya.


Sun watse birni kaza har da kauye

Kowa ta kai nai yake tafiya.


Iyali su watse da dangi hakan nan

Kowa a firgice sai tafiya.


Da muggan diya cikin namu soja

Ba su da niyyar zaman lafiya.


A kauye birane misalin su Baga

Sun yi ta gilla ga baki daya.


Sun kashe yara, sun kona mata

Sun kau da dadin zaman lafiya.


Ta’ala Mashiryi ga ni gare Ka

Ina zanka rokon zaman lafiya.


Gare ni da ’ya’ya da mata dukkanmu

Da dangi abokai ga baki daya.


Musulmi, Kirista Ta’ala Karimu

Hada mu zumuncin zaman lafiya.


Dade mu fahimta ta juna mu gane

Cikin arziki ba kamar lafiya.


Fitinnu na baya kaza na zamanu

Ka kare mu Jalla mu zam lafiya.


Mu rungumi ilmu na dini da dunya

Ci gaban rizku don zaman lafiya.


Dade mu da tsoronKa ya Jalla Sarki

Domin Muhamman mijin Mariya.


Ba mu kadai ba har da Boko Haramun

Yaranmu shirye su baki daya.


kanne da yayye cikinsu gaba dai

Maido su hanyar zaman lafiya.


Ka yafe su laifinsu komai yawansa

BayinKa ne Rabbu Mai lafiya.


Idan Ka tsane su Allahu Gafuru

Waye gare su ko a nan duniya?


Ka nunan da raina ina sintiri

Da nono a Yerwa zaman lafiya.


In je ni Bama in mika caffa

Gidan Mbusube Baba mai gaskiya.


Rabbi Ka kai ni Gwoza in gan su

Mutane na kirkin zaman lafiya.


Askira, Uba, Michika in je

kasashe na Margi mutan lafiya.


In shiga Maiha da Mubi in gan su

In ba su Wakar Zaman Lafiya.


In zo ni Gombi in shiga Hong

Har ma da Song don zaman lafiya.


Ku bar ni in zarce wajen Yola dangi

Filani na Lamido mai gaskiya.


In kwan salati in je ga Inna

Da “Intel” da dukkan maso lafiya.


Nuhu Ribadu aboki amini

Ina mika caffa ga mai gaskiya.


Da safe in je ni school in gane su

Teachers na ilmu cikin lafiya.


Ga yara da manya musamman ga mata

Ci gaba za mui ga baki daya.


In shiga mota in kama hanya

Zuwa Ganye gun su mutan lafiya.


In je ni in gana da danginmu Chamba

Da sarkinsu Gamwari mai gaskiya.


In zo ni Numan, in sheke ayata

Baki na Benuwai zaman lafiya.


Timawus Mathias in ganai har ya kai ni

Gurin nasa gwarzon zaman lafiya.


Sarkin ‘Bata in yi caffa gare shi

In fadi gu nasa mai gaskiya.


Lamurde zan sayi kifi gasasshe

Na cinye a mota zaman lafiya.


Ga Tula sun zo da tarba gare ni

Suna so in rera Zaman Lafiya.


Kaltungo, billiri har ma da Kumo

Ku tashi ku mike zaman lafiya.


Ku wo dandazon sallama don in gan ku

Ku ba ni aron kunnuwan lafiya.


Ku kore su Shaidan ku zan yin zumunci

Ku zauna ku mike cikin lafiya.


Zan shiga Kumo domin in gan shi

Muhammadu Kumo kana lafiya?


In ba su loto da baya tsawaita

Domin in zarce garin gaskiya.


Gombe ta Buba in sadu da dangi

Hausa da Fulbe ga baki daya.