Allah Ya yi wa Sheikh Ishaq Yunus rasuwa
Malamin ya rasu bayan ya sha fama da rashin lafiya.
Fitaccen Malamin Addinin Musulunci nan na Jihar Kaduna, Sheikh Ishaq Yunus Almadany, ya rasu bayan fama da rashin lafiya.
Ya rasu a ranar Alhamis a Asibitin 44 Army Reference da ke Kaduna.
- An tsinci gawar Ɗan Majalisar da aka yi garkuwa a jajibirin Kirsimeti
- Tinubu ya sauke shugabar Jami’ar Abuja, ya yi sauye-sauye a jami’o’in Najeriya
Jami’in hulɗa da jama’a na na kafafen sada zumunta na ƙungiyar Izalatul Bidia Waikamatus Sunnah (JIBWIS), Ibrahim Shehu Giwa ne, ya tabbatar da rasuwar.
Shugaban JIBWIS reshen Jihar Kaduna, Alhaji Adamu Ibrahim, ya bayyana alhininsa, tare da yin addu’ar Allah Ya gafarta masa Ya kuma Aljanna makomarsa.
Masallacin Sultan Bello da ke Kaduna, shi ma ya sanar da rasuwar malamin a shafinsu na Facebook, inda suka yi addu’ar Allah Ya jiƙansa.
Za a yi jana’izarsa da misalin ƙarfe 5 na yamma a filin idi na Sultan Bello, da ke Kaduna.