Amare sun fice daga liyafar bikinsu don zuwa rubuta jarrabawar kammala karatu

Wasdanu amare Dorcas Atsea da Deborah Atoh a lokacin da ake tsakiyar bikin aurensu kwatsam sai aka sanar  dasu cewa a wannan lokacin za su rubuta jarrabawar kammala karatun jami’arsu.  Amaren Dorcas Atsea da Deborah Atoh wadanda dalibai ne da ke karatun fannin aikin jarida a jami’ar jihar Benue, nan take suka fice daga cikin […]

Amare sun fice daga liyafar bikinsu don zuwa rubuta jarrabawar kammala karatu

Wasdanu amare Dorcas Atsea da Deborah Atoh a lokacin da ake tsakiyar bikin aurensu kwatsam sai aka sanar  dasu cewa a wannan lokacin za su rubuta jarrabawar kammala karatun jami’arsu. 

Amaren Dorcas Atsea da Deborah Atoh wadanda dalibai ne da ke karatun fannin aikin jarida a jami’ar jihar Benue, nan take suka fice daga cikin taron jama’ar da suka tara don  bikin nasu a daidai lokacin da madaurin auren  ke tambayersu cewa, suna son junansu a matsayin ma’aurata kuma za su iya rike amanar juna? Da sauran tambayoyi da kuma sharuddan aure da aka yi a wani coci.

Kawai sai ga sanarwar gaggawa cewa jarrabawar da ya kamata su rubuta ta tun a watan Fabrairu yanzu an mayar ranar 7 ga Afrilu wanda ya yi daidai da ranar auren, bayan  duk sun sanar da ranar bikin.

Kafin su fice daga wurin bikin sai da suka canza kayan jikinsu.

Atsea, ya bayyana wa manema labarai cewa an riga an sanya bikin kafin jarrabawar amma mun yi yunkurin a ba mu dama don bayan jarrabawar mu rubuta tamu amma abin ya cutura, don har sai da muka tuntubi malamar gudanar da jarrabawar a karshe sai cewa, ta yi mu zabi aure ko jarrabawa?

UNICEF ta tallafa wa Kano da kayan adana alluran rigakafi

Ambaliya: BUA ya bai wa Maiduguri tallafin biliyan 2

’Yan sanda 5 sun rasu a hatsarin mota a Kano

Tabbas ’yan Najeriya na cikin matsin rayuwa — Kalu