Amurka ta dakatar da bai wa Nijar tallafi

Za a ci gaba da taimakon agajin jin kai na ceton rai da abinci.

Amurka ta dakatar da bai wa Nijar tallafi

Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Anthony Blinken

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken ya sanar da dakatar da wasu shirye-shirye da su kunshi ba da agaji ga Nijar bayan hambarar da zababben shugaban kasar da majalisar soji ta yi.

A karshen makon da ya gabata ne Faransa ta dakatar da duk wani taimakon raya kasa da take bai wa Nijar bayan juyin mulkin da aka yi wa Shugaba Mohamed Bazoum.

Kungiyar Tarayyar Turai da wasu kasashe da dama ma sun dakatar da goyon bayansu.

Duk da haka, “za a ci gaba da taimakon agajin jin kai na ceton rai da abinci” kuma Amurka za ta ci gaba da gudanar da ayyukan diflomasiyya da tsaro don kare jami’anta a kasar, in ji shi.

Nijar na samun kusan dala biliyan biyu a duk shekara a matsayin taimakon raya kasa a hukumance, a cewar Bankin Duniya.

Zaɓen Edo: Duk wanda ya kaɗa ƙuri’a ya koma gida ya zauna — ’Yan sanda

Hotunan yadda Zaɓen Gwamnan Edo ke gudana

An buƙaci mazauna Benuwe su yi ƙaura saboda fargabar ambaliyar ruwa

Abubuwan da ya kamata ku sani game da Zaɓen Edo