An ɗage taron mahaddata Qur’ani da za a yi a Abuja

Tun farko dai an saka ranar Asabar 22 ga watan Fabrairu na 2025 a matsayin ranar da za a gudanar da taron

An ɗage taron mahaddata Qur’ani da za a yi a Abuja

Rahotanni sun nuna cewa an ɗage taron mahaddata al-Qur’ani da ake yi wa laƙabi da Qur’anic Convention a Turance da ya rage ƙasa da mako biyu wanda za a gudanar a Abuja kamar yadda BBC Hausa ta bayyana.

An dai ranar Asabar 22 ga watan Fabrairu na 2025 a matsayin ranar da za a gudanar da taron da ake sa ran zai samu mahalarta waɗanda mahaddata Qur’ani ne sama da dubu 60 daga ciki da wajen Najeriya.

Wani ɗan kwamitin tsara taron wanda bai so a ambaci sunansa ba ya shaida wa BBC cewa, “tun daren jiya Alhamis aka ɗage yin wannan taro.

Sai dai kuma majiyar ba ta tabbatar wa da BBC dalilin da ya sa aka ɗage taron ba da kuma yaushe ne sabon lokacin da za a yi taron a nan gaba.

Majalisar Wakilai ta ba da umarnin rufe shafukan intanet na batsa

Manyan makarantu sun shiga yajin aiki a Adamawa

Sanƙarau ta kashe mutum 26 a Kebbi

Ana fargabar ɓarkewar Sanƙarau a Sakkwato