An ɗauke wutar lantarki a faɗin Najeriya

Wutar lantarki ta dauƙe gaba ɗaya a faɗin Najeriya a safiyar Alhamis.

An ɗauke wutar lantarki a faɗin Najeriya

Turakun Lantarki

Wutar lantarki ta dauƙe gaba ɗaya a faɗin Najeriya a safiyar Alhamis a sakamakon durkushewar babban layin lantarkin kasar.

Hakan na zuwa ne makonni kaɗan bayan kamfanin samar da wutar lantarki na Najeriya (TCN) ya sanar da cikarsa shekara guda ba tare da babban layinsa na lantarki ya samu ɗaukewar wutar gaba ɗaya ba, kamar yadda aka saba a ƙasar.

Wata sanarwa da kamfanin rarraba wutar lantarki na Enugu (EEDC) ya fitar a safiyar ta ce wutar ta fara ɗaukewa ne da misalin ƙarfe 12:40 na dare ne.

Sakamakon haka, “duk tashoshinmu ba su da wutar lantarki da za su raba a jihohin Abia, Anambra, Ebonyi, Enugu da Imo.”

Aminiya ta gano cewa ƙarfin wutar lantarkin kasar ya ragu zuwa megawatt 273 daga cikin biyu daga cikin cibiyoyinta 27.

An ƙaddamar wa ’yan kasuwa sabon tsarin biyan haraji a Gombe

Majalisa na son ƙirƙiro sabbin jihohi 31 a Najeriya

Malamai sun fara yajin aiki a Ebonyi

Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibai