An bukaci kasashen duniya su ja damara wajen yaki da fataucin miyagun kwayoyi

An bukaci  hukumomin duniya  da  su mike tsaye  domin yaki da  fatauci  da kuma shan miyagun kwayoyi, wanda  yake wa  jama’a  da yawa illa. Shugaban kula  da fatauci  miyagun kwayoyi  na  Majalisar dinkin Duniya, Mista Yury Fedetob ne tare da  tsohon shugaba Cif Olusegun Obasanjo, wanda yanzu shi ne  shugaban hukumar  yaki  da  fataucin miyagun […]

An bukaci kasashen duniya su ja damara wajen yaki da fataucin miyagun kwayoyi
An bukaci kasashen duniya su ja damara wajen yaki da fataucin miyagun kwayoyi

An bukaci  hukumomin duniya  da  su mike tsaye  domin yaki da  fatauci  da kuma shan miyagun kwayoyi, wanda  yake wa  jama’a  da yawa illa.
Shugaban kula  da fatauci  miyagun kwayoyi  na  Majalisar dinkin Duniya, Mista Yury Fedetob ne tare da  tsohon shugaba Cif Olusegun Obasanjo, wanda yanzu shi ne  shugaban hukumar  yaki  da  fataucin miyagun kwayoyi  na  kasashen  Afirka  ta  Yamma da  shugaban hukumar  yaki  da  safarar miyagun kwayoyi  na Najeriya suka ba da wannan sanarwar bukata.
Shugabannin  suka  ce  ba kasashen Afirka  ne kadai ke fama da  wannan kalubalen ba,  a’a, kusan duk kasashen duniya  ne,  sai dai wata  kasa ta fi  wata kwazo  da kuma  doka  mai tsanani  game da  wannan mummunar  dabi’ar.  Saboda haka suka ce  kowa  na da tasa gudummawar da zai bayar wajen ganin an fatattaki  wannan  annoba.
Suka ce wannan na daya  daga  cikin dalilan da suka sa  da  yawan kasashen duniya  suke  fama  da  aikata  manya-manya  ayyukan  assha, tare  da  fuskantar  kalubalen  tabarbarewan  tsaro,  wanda haka yana nufin koma baya  ga  duk  wata  al’ummar da ta  samu kanta  cikin wannan yanayi. “Kuma  kowace kasa ta duniya  tana  da karfi  bakin gwargwadon hali  na yadda  za ta  fuskanci  wannan  matsalar,  sai  dai kila rashin shugabannin da suka  mayar  da  hankalin a kan illar  wannan  lamari take hana su tabuka komai”. Inji su.
Wadannan shugabannin  suna  magana  ne  a taro karo  na 57 da aka yi a biana a kan yaki  da  sha  tare  da fataucin miyagun kwayoyi  na duniya.
Sa’ilin da  yake  jawabinsa wajen taron, shugaban hukumar NDLEA,  Alhaji Amadu Giade  ya ce  duk  da  yake Najeriya na bakin kokarinta, amma rashin wadattaun kudin tafiyar da hukumar ya zame karfen kafa, wanda  da  tuni  kasar  ta  tsufa  da  fatattakar dillalan kwayoyi  a cikinta.
Shi ko  Mista Fedotob cewa ya yi  fatarsa ya ga cewa kasashen duniya sun baiwa  samar da kwayoyi  ko kuma magunguna nagari fifiko, wanda zai maye gurbin masu amfani da miyagun kwayoyi a matsayin abin biyan bukatarsu. Shi kuma tsohon shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo,  a nasa  jawabin cewa  ya yi  yana  fatar  ganin an shawo  kan hana  masu  hambudar miyagun kwayoyi  ta  hanyoyi  daban-daban,  domin ta  haka  ne ake  kara samun  yawaita  ayyukan assha  cikin al’umma.
Kusan duk wanda  ya yi  jawabi  a wajen  wannan taron,  ba  wanda  bai tabo  bukatar  kara wa  masu  wannan aikin yaki  da  sha  da kuma  fataucin miyagun  kwayoyi  kudin da  za su  iya aiwatar  da  wannan  gagarumin  aiki,  wanda  duk  dan kasa nagari  na da  gudunmawar da  zai  ba da  ta  wannan  fannin.
Daga karshe suka ce  akwai bukatar samar wa matasa aikin yi, musamman a kasashen Afirka  domin kawar da  hankulansu  daga  harkokin shan miyagun kwayoyi.