An ceto hafsan sojin da aka yi garkuwa da shi a NDA
Jami’an tsaron da suka ceto shi sun tarwatsa sansanonin ’yan bindiga.
Kwalejin Horar da Sojoji (NDA)
An ceto Manjo Christopher Dantong, hafsan sojin da ’yan bindiga suka yi garkuwa da shi a makarantar horas da kananan hafsoshin soji ta NDA.
Hadin gwiwar sojoji da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) da sauran hukumomin tsaro ne suka kubutar da Manjo Dantong, a ranar Alhamis, 17 ga Satumba, 2021, bayan sun kashe ’yan bindiga sun kuma tarwatsa sansanoninsu a yankin Afaka zuwa Birnin Gwari na Jihar Kaduna.
- Mu da ma’aikatan gwamnati ba mai son a magance matsalar tsaro —Dan bindiga
- Halin da ’yan bindiga ke ciki bayan katse hanyoyin sadarwa
Da yake tabbatar da hakan, Daraktan Yada Labaran Runduna ta 1 ta Sojin Kasa ta Najeriya, Kanar Ezindu Idimah, ya ce tuni aka kai Manjo Dantong zuwa NDA bayan ya samu kulawa daga wani rauni da ya samu.
A cewarsa, za su ci gaba da share yankin har sai sun kamo wadanda suka kashe hafsoshin domin su fuskanci hukunci.
A ranar 24 ga watan Agusta, 2021 ’yan bindiga suka saci jiki suka kutsa cikin harabar NDA da ke yankin Afaka a Jihar Kaduna, inda suka kashe wasu hafsoshin soji biyu, suka kuma yi awon gaba da Manjo Dantong.