An ceto jaririn da aka sayar mako daya da haihuwarsa

Gwamnatin Jihar Edo ta ceto wani jariri dan kimanin sati daya da haihuwa daga hannun masu cinikin jarirai a tsakanin jihar da kuma Anambra. Kwamishinar Shari’a ta Jihar kuma shugabar kwamitin yaki da safarar mutane a Jihar, Farfesa Yinka Omorogbe ta ce dillalan sun sayar da jaririn a kan N300,000, kuma an gurfanar da su […]

An ceto jaririn da aka sayar mako daya da haihuwarsa

Gwamnatin Jihar Edo ta ceto wani jariri dan kimanin sati daya da haihuwa daga hannun masu cinikin jarirai a tsakanin jihar da kuma Anambra.

Kwamishinar Shari’a ta Jihar kuma shugabar kwamitin yaki da safarar mutane a Jihar, Farfesa Yinka Omorogbe ta ce dillalan sun sayar da jaririn a kan N300,000, kuma an gurfanar da su a kotu domin su girbi abun da suka shuka.

“A ranar 5 ga Agusta, sashen bincike na kwamitinmu ya gano wani gidan da ake amfani da shi wajen cinikin jarirai a jihohin Edo, Anambra da wasu sassan kasar nan.

“Bayan mun kama daya daga cikin dillalan mun titsiye ta, sai ta fada mana sunan wata mata a Jihar Anambra, inda a nan ne gidan cinikin jariran yake”, inji ta.

Ta kuma ce bayan da suka kama matar ta Anambra sai ta shaida wa jami’ansu cewa jaririn da mahaifiyarsa na zaune ne a wani asibiti.

Daga bisani matar ta jagoranci ‘yan kwamitin zuwa asibitin da matar ta haifi jaririn tare da kama unguwarzomar da ke karbar haihuwa a wurin.

Ta ce kwamitin ya gano wata budurwa da ta haihu ranar 28 ga watan Yuli da aka sayar da jaririn nata bisa alkawarin za a ba ta Naira 300,000 a matsayin kasonta.

“Mun kuma samu matar da wata budurwar wacce ke dauke da juna biyu kuma ta kusa haihuwa kuma ta kasa cikakken bayanin makasudin zamanta a gidan”, inji shugabar kwamitin.

Sojoji Sun Kashe ’Yan Boko Haram 23 A Borno

Fasinjoji sun jikkata yayin da tankar mai ta yi bindiga a Abuja

PDP ta yi watsi da sakamakon zaɓen Edo, za ta garzaya kotu

1.5bn kaɗai aka sanya a asusunmu — Tsohon Kwamishinan Sakkwato