An dage bude sufurin jirage na kasa da kasa

An kara da sati daya kuma za a fitar da matakan ramuwar gayya ga kasashe

An dage bude sufurin jirage na kasa da kasa

Jirgi qirar Boeing 737 Max

Gwamnatin Tarayya ta za ta bude zirga-zirgar jiragen sama na akasa da kara a Asabar 5 ga wata Satumba, 2020.

Darekta Janar na Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama (NCAA), Shuaibu Nuhu, ya sanar da karin sati daya daga lokacin da aka sanar da farko, na 29 ga watan Agusta.

A yammacin Alhamis a taron jawabain kwamitin yaki da cutar coronavirus a Najeriya, Shuaibu Nuhu ya ce Najeriya na kokarin aiwatar da dukkanin matakan ramuwa a kan duk kasar da ta hana matafiya daga Najeriya shigar ta, fakewa da cutar coronavirus, ta hanyar tsauraran sharudda kamar yadda su ma suke yi.

“Za a wallafa da cikakken jerin sunayen kasashen da matakin zai shafa tare da matakan na COVID-19 nan ba da jimawa ba”, inji shi.

A baya Aminiya ta kawo muku rahoto inda Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika ya ce za a dawo da jigilar kasa da kasa a ranar 29 ga watan Agusta.

Kari na tafe…