An fara koyar da harshen Mandarin na China a makarantun Legas – Kwamishina

An fara  koyar  da harshen Mandarin na kasar China  a wasu  makarantu biyar da ke Jihar  Legas,  domin bunkasa  koyon  harsunan  kasashen  duniya, kamar yadda Kwamishinar ilimi  ta jihar,  Madam Olayinka Oladunjaiye    ta  bayyana    wa  taron manema  labarai  kan   sauye-sauye  da ci  gaban  da  aka  samu  a ma’aikatarta.Kwamishinar  ta ce  makarantun sun hada da   Bolade […]

An fara koyar da harshen Mandarin na China a makarantun Legas – Kwamishina
An fara koyar da harshen Mandarin na China a makarantun Legas – Kwamishina

An fara  koyar  da harshen Mandarin na kasar China  a wasu  makarantu biyar da ke Jihar  Legas,  domin bunkasa  koyon  harsunan  kasashen  duniya, kamar yadda Kwamishinar ilimi  ta jihar,  Madam Olayinka Oladunjaiye    ta  bayyana    wa  taron manema  labarai  kan   sauye-sauye  da ci  gaban  da  aka  samu  a ma’aikatarta.
Kwamishinar  ta ce  makarantun sun hada da   Bolade Junior Grammer  School da Ikeja  Junior Grammer Schiool da Immaculate High Comprehensibe da New Era Junior Girls School, da  aka  fara  koyar da  harshen kasar Sin, sai kuma  makarantar Birch Freeman Senior High School, wadda  aka  fara  koyar  da  harshen  Jamusanci.
Madam Olayinka  ta ce  gwamnati  ta fito  da  wannan tsarin ne   domin  ta  kara  yawan harsunan da ake koyarwa  a makarantu,  sannan duk dalibin  da ya yi fice  a daya dagas  cikin  harsunan  sai  gwamnati  ta kara  masa  kwarin gwiwa  domin ya  karanta  shi   zuwa  matakin karatu  na gaba, wanda  har  idan  ta kai  ya tafi  daya  daga  cikin  kasashen  da ake magana da  harshen.
Ta ce za a kara  yawan  makarantun ne ganin yadda  ake  samun yawan  daliban da  suka  suna  sha’awar  koyon  harsunan. Game da karin kudin  makaranta  a  jami’ar  Jihar Legas,  Kwamishinar  ta  ce  ba  kanshin gaskiya  a cikinsa,  domin wadanda  suke  korafin   sun kasa  biya, gwamnati  ta  taimaka musu  da kudin makarantar.
Ta ce kuma  gwamnatin jihar  ta bukaci  daliban  da su je  su yi  shawara  nawa  suke  ganin  za su  iya  biya  a matsayin kudin makaranta,   idan har sun ce wanda  gwamnati  ta  dan kara  ya yi  yawa, kuma har  yanzu  su  ake  jira,   domin gabatar  da  wannan  matsaya  da  suka  cimmawa,  ‘za ta  duba  da  idon  basira.’
Kwamishinar  ta  yaba   nasarar  da aka samu  a makarantar koyon  sana’a  da  gwamnatin  ta  bude,  wadda  da  farko  da kyar  aka  samu  dalibai  cikinta  yau  tana da  dalibai  250,  kuma  sun yi  rawar  gani  a jarrabawar  farko  da  suka  yi  inda  kashi  98 cikin 100  ne  suka  samu  nasara.