An fi kamuwa da cutar Ebola daga 1 gawa – Hukumar WHO

Shugaban kasa Jonathan Goodluck ya bayyana cewa daga bayanan da ya samu, kashi 60 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar Ebola, sun samu cutar ne ta hanyar hulda da gawa a yayin da suke kokarin yin jana’izarta, saboda haka ya bukaci ’yan Najeriya su rika lura a yayin gudanar da jana’izar ’yan uwansu.Ya […]

An fi kamuwa da cutar Ebola daga 1 gawa – Hukumar WHO

Shugaban kasa Jonathan Goodluck ya bayyana cewa daga bayanan da ya samu, kashi 60 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar Ebola, sun samu cutar ne ta hanyar hulda da gawa a yayin da suke kokarin yin jana’izarta, saboda haka ya bukaci ’yan Najeriya su rika lura a yayin gudanar da jana’izar ’yan uwansu.
Ya ci gaba da cewa, bayanai sun nuna cewa marigayi Patrick Sawyer da ya shigo Najeriya da cutar Ebola daga kasar Liberiya ya kamu da cutar ce a lokacin da yake binne ’yar uwansa da ta rasu ta hanyar cutar. Kuma maimakon ya bari a bincike shi, sai kawai ya taho Najeriya ya yada cutar ga wadansu.
Dangane da haka ne Shugaba Jonathan ya ce zai fi dacewa mutane su rika binne gawa a wurin da mamacin ya rasu maimakon daukarta daga wani bangare zuwa wani bangare na kasar nan.
Ya kara da cewa, wadanda suke son dole sai sun yi bikin binne gawar suna iya dakatar da yin haka har zuwa lokacin da za a shawo kan cutar ta Ebola, sai su fito da gawar su sake yi mata jana’iza irin wadda suke so.
Ya bayar da misali da abin da ya faru a cikin al’ummarsa lokacin yana makarantar sakandare inda aka yi sakaci wajen kula da wani wanda cutar kwalara ta kama shi, daga bisani cutar ta kusan cinye daukacin al’ummar yankin.
Shugaban ya ce, “Na tattauna da mutane da dama a ciki da wajen kasar nan tun lokacin da cutar Ebola ta bulla, kuma a tattaunawar da na yi da babbar darektar hukumar lafiya ta Majalisar dinkin Duniya (WHO) Misis Maget Chan, ta ce daga binciken da suka gudanar, kashi 60 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar Ebola sun samu cutar ne a lokacin da suke rufe gawa.”
“Shi ya sanya da wannan babbar darektar ta hukumar WHO ta yi mini wannan bayanin na ga ya kamata mu shawarci mutane su dakatar da bikin binne gawa. Saboda haka muna kira ga shugabannin addini da su dakatar da mafi yawan abubuwan da suke yi a yayin binne gawa, mu rika sauraron shawarwarin masana harkar kiwon lafiya domin mu tsirar da mutanenmu.’’
Jonathan ya bayyana cewa, “Idan muka yi abin da ya kamata game da cutar Ebola, za mu iya shawo kan matsalar a cikin watanni biyu, sai mu cigaba da gudanar da rayuwarmu yadda muka saba.’’
Shi ma Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar  ya bukaci musulmi, a wata sanarwa da Sakataren Jama’atu Nasril Islam, Dokta Khalid Aliyu ya sanya wa hannu, cewa su rika kaffa-kaffa a yayin da suke jana’iza kuma su kula da tsabtar muhallinsu da masallatansu, kamar yadda addinin Musulunci ya tanadar.
Jami’in baki na kungiyar ECOWAS, wanda shi ma ya kamu da cutar a sakamakon cudanya da ya yi da marigayi Mista Patrick Sawyer lokacin da ya shigo kasar nan a ranar 20 ga watan Yuli, ya rasu ranar Talata, wanda ya sanya ya zama mutum na uku da ya rasu a Najeriya a sakamakon kamuwa da cutar, sauran biyun su ne, Mista Patrick Sawyer da kuma wata jami’ar jinya.
A halin yanzu dai an rufe ofishin ECOWAS da ke Legas, a yayin da kuma aka sanya ma’aikatan ofishin a cikin mutane 170 da ake lura da su saboda cudanya da suka yi da Mista Sawyer.

Kilishi ba ya haifar da Ebola   –Dokta Nasir Gwarzo

Daga Abubakar Ibrahim, a Legas

Sabanin jita-jitar da ake yayatawa cewa wai ana iya samun cutar Ebola daga cin nama Kilishi, shugaban yaki  da  wannan cutar  na  kasa,  Dokta  Nasir Sani Gwarzo  ya ce  wannan batu babu  kamshin gaskiya  a cikinsa,  domin ba a samun wannan cutar  ta  dabbobin gida  ko kuma  a  nama dafaffe  ko  gasasshe.
Ya ce  ko  a dabbobin dajin ma  sai  a wadansu  daidaiku  ne ake samu,  kuma  su ma  sai ta  hanyar mu’amala da  jininsu ko  ruwan da ke  jikinsu,  amma  batun cin kilishi  a kamu  da  wannan cutar,  wannan babu  gaskiya  cikinsa  ko  kadan.
Doktan  ya  shaida wa  wakilinmu cewa  mutane  su  saki  jiki  su ci  kilishi  domin babu cutar  Ebola  a  cikinsa.
Ya ce  tun daga  ranar  da gwamnatin  tarayya  ta fara  yaki  da  wannan cutar,  kullum  sai  ta  tantance  masu  shigowa  kasar  kafin  ta  bar su, domin ko  sai an yi wa  mutum  gwajin zafin jiki  mai  nasaba  da  cutar  tukunna  kafin a  bar shi  ya  shigo.
Dokta  Nasir  ya ce  ko  a  ranar Litinin, sai da  aka yi  wa mutane  kusan 500  gwaji  tsakanin bakin iyakar Najeriya  da Jamhuriyar Benin,  haka  kuma mutane  985 aka yi  musu  irin  wannan gwajin a  filin jirgin  saman Nmamdi Azikwe  da ke  Abuja  kafin a  bari  su  shigo  cikin Najeriya,  kuma  duka  an yi  sa’a  babu wanda  zafin jikinsa  ya  wuce  abin da  ake  tsoro.
Sai  dai ya ce  ba  duka  bakin  iyakokin ake  wannan gwajin ba,  domin  har  yanzu  ba a samu  wadatattun wadannan  kayan  awon  ba,  amma  yana  fata  cikin  wannan  makon a  samu  wadatattun  kayayyakin,  kuma  da  zarar  sun samu,  hatta  masu  gittowa ta wadannan iyakokin  da  kafa  su ma  za a  rika yi  musu  wannan gwajin.
  Dokta Nasir ya ce  biyar  daga  cikin mutane takwas da aka killace ana kula da su saboda kamuwa da cutar  suna  samun sauki  kwarai  da  gaske,  su ma  sauran  ukun  ana fata  su  samu  sauki  nan ba da  jimawa  ba.
Likitan ya kuma  shawarci  masu kwankwadar  ruwan  gishiri da  su  daina,  domin  suna  kara  dagula  harkokin  kiwon lafiyarsu  ne, saboda  babu  wani wurin da  aka  samo  cewa shan ruwan gishiri  yana maganin cutar Ebola. Wadanda  kuma  ba su  bari  ba,  to  su  kwana  da  sanin cewa  suna kara  tura  kansu  cikin matsala ne.

Mutane sun cigaba da shan ruwan gishiri a Legas

Abubakar Haruna, Daga Legas da Husaini Isa, a Jos

Duk da kiraye-kirayen da likitoci suka rika yi da shawarar da Hukumar Lafiya ta Majalisar dinkin Duniya (WHO) ta bayar na mutane su guji yin amfani da ruwan gishiri don maganin cutar Ebola, binciken Aminiya ya gano cewa mazauna Jihar Legas sun ci gaba da sha tare da yin wanka da ruwan gishirin.
Mutane da dama da Aminiya ta tattauna da su a jihar sun bayyana cewa suna ci gaba da yin amfani da gishiri saboda imanin da suka yi cewa kariya ne daga cutar.
Malam Mustafa Sani cewa ya yi, “Gaskiya ban daina shan ruwan gishiri ba kuma ban daina wanka da shi ba. Saboda ni na yi imani kuma na yarda da wadanda suka fada mini cewa na rika wanka da shi Allah zai kare ni daga kamuwa daga cutar Ebola. Kuma ai shi da ma gishiri magani ne mutane ne ba su ankara ba tun tuni sai yanzu da suka ga haza”.
Malama Maimuna Muhammadu kuwa cewa ta yi, “Ni har yanzu ina wanka da shi saboda malamai ne suka fada mana suka ce mu karanta kulhuwallahu kafa 41 da kula’uzai a cikin ruwan mu sha kuma mu yi wanka. Saboda haka zan ci gaba da yin amfani da gishirin har sai malamanmu sun ce mu dakata”.
Shi ma Malam Sule Tanko cewa ya yi, “Ina ci gaba da yin wanka da gishiri, saboda na yarda kariya ne daga kamuwa daga cutar Ebola. Tunda na fara wanka da shi na samu natsuwa kuma na ji canji a jikina, duk da ba shi da dadin sha, amma duk da haka mu mun yarda yana magani”.
A kalla mutane sama  20 ne aka kwantar a asibitoci daban-daban na garin Jos, babban birnin Jihar Filato, a  makon da ya gabata, sakamakon shan ruwan gishiri don rigakafin cutar  Ebola.
Mutane da dama a jihar sun yi ta shan ruwan gishiri tare da yin wanka da shi a  ranar Alhamis din makon da ya gabata.
Kwamishinan lafiya na Jihar Filato, Dokta Fom Dakwak, wanda babban sakataren ma’aikatar lafiya ta jihar,  Dokta Elias Pede ya wakilta, ya yi bayanin cewa ruwan gishiri ba shi da wata alaka da warkarwa ko riga-kafin cutar.