An gano gawar shugaban Fulani a rijiya a Filato 

Muna kira ga daukacin mambobinmu da su kwantar da hankalinsu, kada su dauki doka a hannunsu.

An gano gawar shugaban Fulani a rijiya a Filato 

An gano gawar wani shugaban Fulani da ya bace, Umar Ibrahim, a wata rijiya a unguwar Jokom da ke garin Mangu na Karamar Hukumar Mangu ta Jihar Filato.

Marigayi Ibrahim shi ne Ciroma na gundumar Kumbun a Karamar Hukumar Mangu.

Kakakin rundunar ‘Operation Safe Haven’ (OPSH) da ke aikin tabbatar da zaman lafiya a jihar, Kyaftin Oya James, ya tabbatar da faruwar lamarin.

A halin da ake ciki, shugaban kungiyar Gan Allah Fulani (GAFDAN), ya bayyana cewa Ibrahim ya bace ne lokacin da ya fito daga asibiti a ranar Laraba don siyo wa matarsa abinci da ke garin Mangu amma bai dawo ba sai da yammacin ranar Lahadi da aka tsinto gawarsa a cikin rijiyar.

Shugaban kungiyar na jihar, Garba Abdullahi ya ce, “Ya ziyarci matarsa da ba ta lafiya da ke Mangu.

“Ranar Laraba misalin karfe 6 na yamma ya fita ya siyo mata abinci amma bai dawo ba.

“Bayan an shafe kwanaki hudu ana nemansa, an tsinci gawarsa a wata rijiya a kusa da asibitin.

“An tsinto gawar ce a gaban sojojin da ke aiki da rundunar ‘Operation Safe Haven’ da ke tabbatar da zaman lafiya a yankin.

“Sai dai duk da faruwar wannan lamari muna kira ga daukacin mambobinmu da su kwantar da hankalinsu, kada su dauki doka a hannunsu.

“Ya kamata mu ci gaba da zama masu bin doka. Hukumomin tsaro suna yin iya kokarinsu.

“Kiranmu ga jami’an tsaro shi ne kawai su kamo wadanda suka aikata wannan ta’asa domin a hukunta su.”

HOTUNA: Yadda aka yi jana’izar Haruna Zago a Kano

NHIS: Kotu ta ɗage bayar da belin Farfesa Yusuf zuwa 27 ga Fabrairu

Sojoji sun doki ’yan sanda kan kama ‘mai laifi’

Miƙa makaman ’yan bindigar Katsina ya bar baya da ƙura