An gurfanar da likita ya yi wa matar aure fyade a asibitinsa

An gurfanar da wani likita a jihar Adamawa a gaban kotu bisa zargin yi wa wata matar aure fyade.

An gurfanar da likita ya yi wa matar aure fyade a asibitinsa

Fyade

An gurfanar da wani likita a Jihar Adamawa a gaban kotu bisa zargin yi wa wata matar aure fyade.

Likitan, wanda ma’aikaci ne a Asibitin Kwararru na Jihar da ke Yola, ana zarginsa ne da aikata lalatar a wani asibiti mallakinsa yayin da yake kokarin yi mata gwajin lafiya.

’Yan sanda masu shigar da kara sun gurfanar da shi a gaban Kotun Majistare a birnin Yola ranar Alhamis bisa zargin cin zarafin matar.

A zaman kotun na farko dai, Mai shari’a Aliyu Babawuro ya dage sauraron karar har zuwa 26 ga watan Nuwamba.

Kakakin Rundunar ’Yan Sanda na Jihar ta Adamawa, DSP Sulaiman Nguroje ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce, “Wacce aka yi wa fyaden ce ta shigar da karar wanda hakan ne ya sa jami’anmu suka tashi tsaye domin gudanar da bincike.

“Matar ta shaida mana cewa lamarin ya faru ne lokacin da ta je asibitin ita da mijinta domin neman lafiya.

“Daga nan ne sai muka gayyaci likitan domin ya amsa tambayoyi, daga bisani kuma muka gurfanar da shi gaban kuliya”.

Boko Haram sun ƙone makarantu a Borno

Har yanzu ’yan bindiga ba su saki matar Manjo Janar Rabe ba

An binne gawar Manjo Janar Rabe a Katsina

Wasu tsiraru ne ke rura matsalar tsaro a Najeriya — Christopher Musa