An harbe barawon akwatin zabe ya mutu a Akwa Ibom
Sojojin da suke lura da zabukan garin Ukanafun sun sanar da rahoton kashe wani barawon akwatin zabe da ya saci akwatin rumfar zaben Ikot Udo Ossiom da ke karamar hukumar Ukanafun a jihar Akwa Ibom. Wata ganau mai suna Misis Elijah ta bayyanawa wakilinmu cewa, mutumin da aka harbe ya yi yunkurin sace akwatin zaben […]
Akwatin zabe
Sojojin da suke lura da zabukan garin Ukanafun sun sanar da rahoton kashe wani barawon akwatin zabe da ya saci akwatin rumfar zaben Ikot Udo Ossiom da ke karamar hukumar Ukanafun a jihar Akwa Ibom.
Wata ganau mai suna Misis Elijah ta bayyanawa wakilinmu cewa, mutumin da aka harbe ya yi yunkurin sace akwatin zaben da safiyau yau bayan ma`aikatan sun kawo kayan zaben rumfar, sai sojojin suka dakatar da shi daga harabar rumfar.
Misis Elijah, ta kara da cewa mutumin ya sake dawo wa karo na biyu da nufin sace akwatin rumfar zaben nan ta ke sojojin suka harbe shi.