An kama barawon wayan da ya caka wa budurwa wuka a Yobe

Barawon da ya caka wa wata budurwa wuka ya kwace wayarta a garin Damaturu na Jihar Yobe ya fada komar ’yan sanda.

An kama barawon wayan da ya caka wa budurwa wuka a Yobe

‘Yan sanda

Barawon da ya caka wa wata budurwa wuka ya kwace wayarta a garin Damaturu na Jihar Yobe ya fada komar ’yan sanda.

A kwanakin baya ne dai wani barawon waya ya kwace wayar budurwar bayan da ya caka mata wuka a gidan baya a unguwar Malari a garin Damaturu fadar.

Sakamakon haka aka garzaya da ita babban Asibitin koyarwa na jihar inda a halin yanzu take samun kulawa.

A wata sanarwa, kakakin ’yan sandan jihar ta Yobe, ASP AbdulKareem Dungus ya ce jami’an su sun kama matashin.

A cewarsa, wayar da barawon ya kwace samfurin Itel ce hade da da layi a ciki.

Dungus ya ce za a ci gaba da bincike daga bisani a tura matashin zuwa kotu don fuskantar hukuncin da ya ya daidai da laifinsa, domin hakan zama izina ga na baya.

Dangote ya karya farashin man fetur

An miƙa wa Majalisar Kano ƙorafin ƙara wa’adin manyan ma’aikatan gwamnati

Matasa 150 Sun Halarci Gasar Kirkire-Kirkiren Fasaha a Kano

APC ta kori tsohon Gwamnan Osun, Aregbesola daga jam’iyyar