An kama dan bindigar Katsina zai kafa sansani a Kano
Dubunsa ta cika bayan ya gudo daga yankin Malumfashi da makamai da kuma dabbobin sata
Kwamishinan ’yan sandan jihar Kano, Mohammed Usaini Gumel
’Yan sanda sun cafke wani dan bindiga inda suka kwato shanun sata 55 a hannunsa a Karamar Hukumar Karaye ta Jihar Kano.
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kano, Usaini Muhammad Gumel, ya bayyana cewa ɗan ta’addan ya tabbatar musu cewa dubunsa ta cika ne a yayin da yake kokarin dawowa jihar Kano da zama.
Dan bindigar, wanda ba a bayyana sunansa ba, ya ce, ya gudo ne daga sansanin ’yan bindiga ta Maidaro ne da ke Malumfashi a Jihar Katsina, ya biyo ta Birnin Gwari a Jihar Kaduna ya shigo Kano.
Ya kuma bayyana cewa ya gudo daga Malumfashi ne sakamakon fadan gungunsu sa na jagoran ’yan bindiga Boderi Isiya.
- Kotu ta sa ranar sauraren rokon daukaka kara kan hukuncin kisan Abduljabbar
- Saurayi ya fille kan budurwarsa a Bayelsa
A cewar dan ta’addan, an kashe jagoran bangarensu da mataimakinsa a fadan, shi ne ya gudo da shanu 55 da tumaki shida da bindigogi uku kirar AK-47, zai koma dajin kananan hukumomin Karaye da Gwarzo na Jihar Kano da zama.
Kwamishinan ’yan sandan ya shaida wa ’yan jarida a ranar Litinin cewa wanda ake zargin ya tabbatar wa ’yan sanda masu bincike cewa an sha zuwa da shi yin garkuwa da mutane a jihohin Katsina da Zamfara da kuma Kaduna.