An kama likita kan laifin yin tsafi da sassan jikin mutum

Wani likita mai suna Dokta Babawale Funsho Joshua, ya shiga hannun ’yan sanda bisa tuhumar yanke sassan jikin gawar wani yaro a jihar Ogun.Babawale, wanda aka kama tare da wasu abokan huldarsa su uku, shi ke da asibitin Ajike Medical Centre da ke Sango Otta a Jihar Ogun.Jami’in hulda da jama’a na hukumar ’yan sanda […]

An kama likita kan laifin yin tsafi da sassan jikin mutum
An kama likita kan laifin yin tsafi da sassan jikin mutum

Wani likita mai suna Dokta Babawale Funsho Joshua, ya shiga hannun ’yan sanda bisa tuhumar yanke sassan jikin gawar wani yaro a jihar Ogun.
Babawale, wanda aka kama tare da wasu abokan huldarsa su uku, shi ke da asibitin Ajike Medical Centre da ke Sango Otta a Jihar Ogun.
Jami’in hulda da jama’a na hukumar ’yan sanda na jihar, Muyiwa Adejobi ya ce an kama shi ne bisa tuhumar hada kai da wasu wajen yanke sassan jikin wani yaro dan wata 13 da ya mutu a asibitinsa ranar takwas ga Yunin bana.
Tuni aka kai gawar jaririn zuwa mutuwaren babban asibitin Ifo, don gudanar da binciken musababbin mutuwarsa. Sauran mutum uku da aka kama su tare da likitan sun hada da Oguntunde Opeyemi da Olaide Adeyanju da Temitope Muraina.

An buƙaci mazauna Benuwe su yi ƙaura saboda fargabar ambaliyar ruwa

Abubuwan da ya kamata ku sani game da Zaɓen Edo

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda