An kama magidanci kan kashe matarsa a Adamawa

Magidanci mai shekaru 40 ya yi wa matarsa kisan gilla a Jihar Adamawa.

An kama magidanci kan kashe matarsa a Adamawa

’Yan sanda sun kama wani magidanci bisa zargin yi wa matarsa kisan gilla a Jihar Adamawa.

Rundunar ’yan sandan jihar ya ce  mutumin dan shekara 40 dan asalin garin Bode da ke karamar hukumar Shelleng na jihar  ne.

Ana zargin bayan ya kashe matar mai suna Godiya Akwale, sannan ya kulle gawarta a cikin gidansu kafin ya tsere zuwa Jihar Ondo.

Ma’auratan sun yi aure sama da shekara uku.

Kakakin ’yan sandan jihar, SP Suleiman Yahaya Nguroje ya tabbatar wa Aminiya kama wanda ake zargin.

Ya bada tabbacin za a gurfanar da shi a gaban kotu bayan kammala bincike.

Osimhen ya maka ɗan jarida a kotu

Abba ya karrama fitattun Kanawa 35

Asibitin Malam Aminu Kano ya hana motoci masu baƙin gilas shiga harabarsa

Mahaifin ma’aikacin Aminiya ya rasu