An kama mahaukaciya da bindigogi a Legas

An kona mahaukaciyar karyar bayan an kama ta da sassan jikin dan Adam.

An kama mahaukaciya da bindigogi a Legas

Wasu bindigogi da aka kwace a hannun wasu ‘yan bindiga a watannin baya a yankin Zamfara da Katsina.

Fusatattun matasa sun kona wata mahaukaciya kurmus bayan an same ta da bindigogi kirar AK 47 guda hudu.

Jama’ar unguwa sun ce an kuma gano sassan jikin dan Adam a tare da mahaukaciyar karyar da ke zamaa karkashin wata gada.

Ana kuma zargin bindigogin da aka kama a wurinta na ’yan fashi ne da ke ba ta ajiya.

Dubun matar wadda ke yin shiga a matsayin mahaukaciya ya cika ne a safiyar Litinin a unguwar Abule-Ado da ke Badagry a Jihar Legas.

Wani matashi da ke zaune a daura da yankin mai suna Abdullahi Alkanawiy, ya shaida wa Aminiya cewa a lokacin da lamarin ya faru ya zo wucewa ta wajen a mota sai ya tarar an banka wa matar wuta.

“Na tsaya na tambaya sai ake fada mini cewa an same ta da bindigar AK 47 guda hudu; Matar sananniya ce, duk wanda yake wucewa ta wajen zai rika ganin ta a karkashin gada, da ka gan ta ka ga mahaukaciya,” inji shi.

Aminiya ta yi kokarin jin ta bakin kakain Rundunar ’Yan Sanda na Jihar Legas, Olamuyiwa Adejobi, amma bai daga waya ba, bai kuma amsa rubutaccen sakon da wakilinmu ta tura masa ba.

Okpebholo ya lashe zaɓen Gwamnan Edo

HOTUNA: Yadda bikin Takutaha ya gudana a Kano

Zaɓen Gwamna: APC ta kama hanyar lashe zaɓen Edo

Zaɓen Edo: INEC ta dakatar da tattara sakamako