An kama mai ƙera wa bata-gari makamai a Jigawa

Ya tabbatar mana da cewa ya kera makamai da dama kuma bai san adadin mutanen da ya sayarwa ba.

An kama mai ƙera wa bata-gari makamai a Jigawa

’Yan sanda. (Hoto: NAN)

Rundunar ’yan sanda a Jihar Jigawa ta samu nasarar kama wani mutum dan shekara 50, da take zargi da kera makamai a Karamar Hukumar Ringim.

Kakakin rundunar a jihar, mukaddashin sifuritendan ‘yan sanda Lawan Shisu ne ya tabbatar da hakan ranar Alhamis.

A cewar Shisu, sun kama mutumin ne a ranar 16 ga watan da muke ciki.

“Rundunar ’yan sanda da hadin gwiwar ’yan sa-kai sun kama wanda muke zargi da kera wa bata-gari makamai a garin Yandutsen Kawari,” inji Kakakin ’yan sandan.

A binciken da aka gudanar a gidansa, an samu kananan bindigu biyu kirar gida, da kuma wasu manya biyu.

Shisu ya ce wanda suke zargin, da kansa ya tabbatar musu cewa yana kera makamai da dama, kuma sau tari bai san wadanda yake sayarwa ba.

SP Lawan Shisu ya ce da zarar sun kammala bincike za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu.

Majalisa ta tsayar da ranar sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin Dokar Haraji

Abba ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaro ta Kano

Za a binciki INEC kan jinkirin gudanar da zaɓen cike giɓi

Gubar harsashi ta jikkata mutane dama a Zamfara