An kama mai shekaru 52 da dala miliyan 4.7 na jabu a Abuja

An yi yunkurin sace kusan naira biliyan 2.7 na tattalin arzikin Najeriya.

An kama mai shekaru 52 da dala miliyan 4.7 na jabu a Abuja

Mutumin da aka kama da jabun daloli

Jami’an Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta NDLEA sun kama wani mutum mai shekara 52 da makudan daloli na jabu a Abuja, babban birnin Najeriya.

Sanarwar da hukumar ta fitar ta ce an yi yunkurin sace kusan naira biliyan 2.7 na tattalin arzikin Najeriya ta hanyar tura kudaden na jabu a kasuwa da suka kai sama da dala miliyan 4.7.

Hukumar ta ce jami’anta sun kama kudaden a yankin Abaji da aka dauko daga Legas zuwa Abuja.

Da yake zantawa da manema labarai a ranar Lahadi, Femi Babafemi, ya ce an kama wanda ake zargi da fataucin kudin mai suna Abdulmumini Maikasuwa.

Hukumar ta ce shugabanta Birgediya Janar Buba Marwa ya bayar da umarnin a mika kudaden da wanda ake zargi ga hannun Hukumar Yaki da Masu Yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta EFCC domin ci gaba da bincike.