An kama matashi kan satar Al-Kur’anai a masallaci a Zariya

Ya kuma shaida musu cewa ya sayar da Alkur’anai akalla 57 ga wani mutum, wanda a halin yanzu ake nema.

An kama matashi kan satar Al-Kur’anai a masallaci a Zariya

Jami’an tsaro na KADVIS sun kama wani matashi da ya addabi masallatai da satar Alkur’ani a yankin Zariya, Jihar Kaduna.

Dubun matashin ta cika ne a masallacin Gamandi Kofar Galadima da ke Zariya inda aka same shi da Alkur’anai tawkas da suma littafin Askari gida guda.

A lokacin da jami’an KADVIS suke tuhumar shi, wanda ake zargin ya amsa cewa ya dade yana satar littafai a masallatai daban-daban.

Ya kuma shaida musu cewa ya sayar da Alkur’anai akalla 57 ga wani mutum, wanda a halin yanzu ake nema.

Bayan titsiye wanda ake zargin, jami’an na KADVIS sun yi nasarar tatsar bayan bayanai kan wanda ke sayen littafan satan a hannunsa.

Tinubu zai tafi Faransa daga nan ya zarce Habasha

NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana

Jami’ar ABU da ke Zariya ta yi sabon shugaba

An soma rigimar haraji tsakanin China da Amurka