An kama mutanen da ‘suka ci balangun gawar ‘Yan sanda’

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Oyo ta damke mutanen da ake zargin sun yanki naman gawar ‘yan sanda suka cinye a lokacin zanga-zangar #EndSARS. Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Kakakin Rundunar ‘Yan Sanda na jihar, SP Olugbenga Fadeyi, ya fada wa Aminiya a yanzu haka an kai su Hedikwatar ‘Yan sanda da ke Abuja don ci […]

An kama mutanen da ‘suka ci balangun gawar ‘Yan sanda’

Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya Mohammed Adamu

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Oyo ta damke mutanen da ake zargin sun yanki naman gawar ‘yan sanda suka cinye a lokacin zanga-zangar #EndSARS.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Kakakin Rundunar ‘Yan Sanda na jihar, SP Olugbenga Fadeyi, ya fada wa Aminiya a yanzu haka an kai su Hedikwatar ‘Yan sanda da ke Abuja don ci gaba da gudanar da bincike.

Daga cikin wadanda aka kama, an ce wata mata ‘yar shekara 34 ta yanki tsokar gawar dan sanda ta cinye.

Sai dai kuma ta ki amincewa da zargin a lokacin da ake gudanar da bincike, amma ta ce wani mutum dan shekara 43 ya ba ta gasasshen naman domin ta ajiye masa.

Da ya ke kare kansa, abokin laifin nata ya amince yana wajen da aka kashe ‘yan sanda tare da wasu ‘yan daba, amma matar ta yanki gawar ta roke shi ya ba ta hankici ko tawul ta kunshe naman a ciki.

Jami’an sun hadu da ajalinsu ne bayan an kai su birnin Badun aikin kwantar da tarzomar #EndSARS a ranar 22 ga watan Oktoba.

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 8, sun ceto mutum 16

APC ta lashe duk kujerun kananan hukumomi a zaben Sakkwato

Sojoji sun kama ’Yan Yahoo 150 a kusa da bariki a Delta

Tinubu ya fara shirin sauke wasu ministocinsa