An kama shanun sata 12 a kasuwar Oko-Oba

Shugabannin kasuwar shanu ta Oko-Oba  sun  kama shanu 12 da  suke  tuhumar na sata ne.Da yake wa taron manema labarai  jawabi, sarkin kasuwar, Alhaji Bello dan-Mubaffa ya ce sun kame shanun ne sa’ilin  da  wata  mota  mai  dauka  shanu 15 ta shigo da su cikin kasuwar, kuma suka tuhumi cewa na sata ne.Ya ce abin […]

An kama shanun sata 12 a kasuwar Oko-Oba

Shugabannin kasuwar shanu ta Oko-Oba  sun  kama shanu 12 da  suke  tuhumar na sata ne.
Da yake wa taron manema labarai  jawabi, sarkin kasuwar, Alhaji Bello dan-Mubaffa ya ce sun kame shanun ne sa’ilin  da  wata  mota  mai  dauka  shanu 15 ta shigo da su cikin kasuwar, kuma suka tuhumi cewa na sata ne.
Ya ce abin da ya kai su ga tuhumar cewa shanun sata  ne shi ne ganin yanayin shanun, wadanda biyar daga cikinsu  suna da ciki, kuma 11 duk karsanoni ne (wato mata matasa masu karfi a jika) da ba kasafai Bafillace zai sayar da su ba.
Sarkin ya ce ganin haka ne sa’ilin da aka kawo su  suka nemi direban da ya kawo su  domin ya yi musu bayanin inda ya fito da ko kuma  ina mai su yake, amma cikin dan kankanen lokaci, sai  direban da motarsa suka yi layar zana,  aka neme su, kasa  ko sama, aka rasa, lamarin da ya kara  tabbatar  musu  cewa shanun na sata ne.
Ya ce, “Har  yanzu da nake muku wannan  jawabi,  ba  wanda ya zo ya ce shanun nan nasa ne,  bayan kwanaki 6  da tsare su.
Saboda haka za mu ci gaba da tsare shanun da ciyar da su. Mun sanar  da ’yan sanda,  wadanda  suka  zo  suka  ga  shanun kuma  suka  ce mu ci  gaba da  ajiye  su  har  sai  an samu  wanda  ya zo  ya ce  nasa  ne,  ko kuma  idan  an  rasa  mai  su  har na tsawon lokaci, hukuma  ta san  yadda  ta yi  da su, sannan a  biya wanda  ya dauki  dawainiyar ciyar da su da lura da su”.
Yayin da manema  labarai  suka  tambayi ko sun  saba  ganin irin haka, sai ya ce, “Ba  shakka  ana  kawo  shanun sata  kuma  muna kamawa  mu mika  su  ga ’yan sanda. Wannan ba  shi ne karo na farko ba, amma  shi ne  karo na farko  da ya dauki  tsawon lokaci wani  bai zo ya ce nashi ba ne. Za mu  ci gsba da  ajiyar  su  har  lokacin da  hukuma  ta  waiwaye  mu”.