An kama shi da kokon kan mutum a makabarta

’Yan sanda sun kama wani mai shekaru 45 da ake zargin matsafi ne dauke kokon kan mutum a garin Abeoluta na Jihar Ogun

An kama shi da kokon kan mutum a makabarta

Mai Laifi

’Yan sanda sun kama wani mai shekaru 45 dauke kokon kan dan Adam a Jihar Ogun.

Ana zargin mutumin yana shirin yin tsafi da kokon kan ne a lokacin da ’yan sanda suka kama shi.

Kakakin ’yan sandan jihar Ogun, Omolola Odutola, ta ce jami’an rundunar sun kama wanda ake zargin ne bayan da ya haka wani kabari ya sare kan gawar da ke ciki domin yin tsafi a garin Abeokua.

Odutola ta sanar a ranar Talata cewa rundunar ta fara gudanar da bincike kan lamarin.

Mutum biyu sun shiga hannu kan zargin sace mahaifiyar Rarara

An ƙone jabun magunguna na N985m a Kano

Sarkin Kaltungo ya koya jama’arsa dabarun noman rogo na zamani

Kasuwar Karu da ke Abuja ta yi gobara