An kama tela da wasu 30 kan zanga-zanga da tutocin Rasha a Kano

An kama telan ne bayan da aka samu tutocin kasar Rasha guda bakwai a wurinsa.

An kama tela da wasu 30 kan zanga-zanga da tutocin Rasha a Kano

’Yan sanda sun tsare wani tela da wasu muane 30 a Kano kan mallaka da kuma daga tutocin kasar Rasha a yayin zanga-zangar tsadar rayuwa.

Hedikwatar ’yan sandan Najeriya na zargin telan da dinka dimbin tutocin Rasha da masu zanga-zanga ke amfani da su a Kano da wasu Jihohin Arewa.

Har ila yau, an kama masu zanga-zangar akalla 30 da ke dauke da tutocin, saboda hakan laifin cin amanar kasa ne.

Kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro ya shirya.

Wasu masu zanga-zangar adawa da mummunan shugabanci a Arewacin Najeriya sun yi ta daga tutar kasar Rasha suna kira gare ta da ta kawo musu dauki.

A karshen makon ne kuma hotunan masu zanga-zangar dauke da tutar Rasha suka yi fara yawo a kafofin sada zumunta.

Hakazalika an ga bidiyon wasu teloli a cikin shago suna dinka tutocin na Rasha, wanda a jikin bidiyon aka rubuta “Gobe babu.”

Washegari, ranar Lahadin Shugaba Tinubu, a jawabinsa ga al’ummar kasar ya gargadi masu zanga-zangar da su guji bari a yi amfani da su wajen cimma wata manufa da ka iya kawo cikas ga cigaban dimokradiyyar Najeriya.

An buƙaci mazauna Benuwe su yi ƙaura saboda fargabar ambaliyar ruwa

Abubuwan da ya kamata ku sani game da Zaɓen Edo

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda