An kashe fararen hula 5 a birnin Timbuktu

Akwai sama da mutum 20 da suka jikkata a harin.

An kashe fararen hula 5 a birnin Timbuktu

Bayanan da ke fitowa daga birnin Timbuktun Arewacin kasar Mali, na tabbatar da salwantar rayukan akalla fararen hula biyar a wani hari na baya-bayan nan da aka kai kan al’umma.

Sabon harin da cikakkun bayanansa ke fitowa a wannan Asabar bayan kai shi a ranar Alhamis, ya zo ne wata guda da rabi bayan kawanyar da mayakan tarzoma suka yi wa Timbuktun.

Tabbacin harin ya fito cikin wata hirar da gwamnan yankin Bakoun Kante ya yi da kafofin watsa labaran cikin kasar, kuma ya ce tuni aka yi jana’izar wadanda suka mutun.

Wasu cibiyoyin lafiya ma dai sun ruwaito cewa akwai sama da mutum 20 da suka jikkata a harin.

Daga cikin wadanda suka salwantan kuma har da wasu kananan yara, kamar yadda shaidu suka tabbatar.

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan

Tags