An kashe sojojin Nijar 6 da ’yan ta’adda 10 a Tillaberi

Sojojin Nijar sun hallaka masu iƙirarin jihadi 10 a garin Sanam da ke yanki Tillaberi

An kashe sojojin Nijar 6 da ’yan ta’adda 10 a Tillaberi

Nijar (AFP)

Sojojin Jamhuriyar Nijar shida sun rasu a wani harin kwanton ɓauna da mayaƙa masu iƙirarin jihadi suka kai musu a ranar Lahadi.
Gwamnatin sojin Nijar ta ce a yayin musayar wutar, dakarun nata sun hallaka 10 daga cikin a mayaƙan da suka kawo musu farmakin a kan babura a garin Sanam da ke Jihar Tillaberi.
Sabuwar gwamnatin sojin ta ƙara da cewa a ranar 9 ga watan nan na Agusta, ’yan ta’adda sun kashe sojoji biyar a garin na Saman da ke iyaka da ƙasashen Burkina Faso da kuma Mali da suke fama da hare-haren ta’addancin masu iƙirarin jihadi.

Shugaban gwamnatin sojin, Janar  Abdourahamane Tchiani dai ya bayyana cewa sun yi wa Shugaba Mohamed Bazoum juyin mulki a ranar 26 ga watan Yuli ne saboda taɓarbarewar sha’anin tsaro a ƙasar.

Zaɓen Edo: Yadda aka kama masu sayen ƙuri’a da ’yan daba

Sarakunan Nijar sun kai wa Gwamnatin Yobe ziyarar jaje

Ɗan majalisa ya yi jinjina kan naɗa Danyaya Sarkin Ningi

’Yan Sanda sun kama gungun ’yan fashi 7 a Katsina