An kashe wani mutum a rikicin APC da PDP a Jigawa

Mutum daya ya rasa ransa sakamakon arangamar da magoya bayan jam’iyyun biyu suka yi da juna.

An kashe wani mutum a rikicin APC da PDP a Jigawa

‘Yan sanda

Akalla mutum daya ne ya rasa ransa, wasu biyar kuma suka jikkata bayan wani rikici da ya barke tsakanin magoya bayan jam’iyyar PDP da na APC a Jihar Jigawa.

Lamarin ya faru ne a lokacin da dan takarar gwamnan jihar na PDP, Mustafa Sule Lamido, ya gudanar da yakin neman zabensa a Karamar Hukumar Maigatari ranar Juma’a.

Rahotanni sun ce bayan isarsu Sakatariyar Jam’iyyar APC, rikici ya barke tsakaninsu da magoya bayan APC.

A cewar sanarwar da ’yan sandan suka fitar, magoya bayan PDP ne suka kai wa wani matashi mai suna Abdullahi Isiyaku, mai shekara 37 da ke zaune a garin Gangare a Maigatari, hari.

An garzaya da shi Babban Asibitin Gumel domin yi masa magani amma daga baya ya mutu sakamakon raunin da ya samu.”

Sanarwar ta kara da cewa, ana gudanar da bincike a sashen binciken manyan laifuka na jihar (SCID) da ke Dutse.

Kakakin rundunar , DSP Lawan Shiisu Adam, ya ce ’yan sanda na bincike domin ganin an gurfanar da wadanda suka aikata laifin a gaban kuliya.

Lamarin da ya haifar da fargaba da tsoro a zukatan mazauna yankin.