An kona ofishin zabe na jihar Abiya

Hukumar ‘yan sanda ta tabbatar da kona ofishin hukumar zabe mai zaman kanta INEC da ke karamar hukumar Isiala-Ngwa ta kudu a jihar Abiya, inda katunan kada kuri’a da dama suka kone  kurmus. Jami’in hulda da jama’a na hukumar ‘yan sanda SP Geoffrey Ogbonna ne ya bayyana wa kamfanin dillancin labarai (NAN) hakan a jiya […]

An kona ofishin zabe na jihar Abiya

Hukumar ‘yan sanda ta tabbatar da kona ofishin hukumar zabe mai zaman kanta INEC da ke karamar hukumar Isiala-Ngwa ta kudu a jihar Abiya, inda katunan kada kuri’a da dama suka kone  kurmus.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar ‘yan sanda SP Geoffrey Ogbonna ne ya bayyana wa kamfanin dillancin labarai (NAN) hakan a jiya Lahadi.

Rahotanni na bayyana cewa, wutar ta fara ne daga bandaki zuwa sauran ofisoshin har zuwa dakin da ake  adana katunan kada kuri’ar zabe.

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan bindiga da tarwatsa 300

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta