An rufe makarantu a Zamfara bayan sace daliban Kankara

Gwamnati ta ce daukar matakin ya zama dole domin kare rayuwar dalibai

An rufe makarantu a Zamfara bayan sace daliban Kankara

Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle

Jihar Zamfara ta rufe makarantunta a yankunan da ke iyaka da jihohin Katsina da Kaduna masu fama da matsalar garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro.

A sanarwar da ta fitar ranar Talata, Gwamnatin Jihar Zamfara ta ce umarnin makarantu 10 ne aka rufe, a matsayin kandagarki, la’akari da yanayin tsaro.

Kwamishinan Ilimin Jihar, Dokta Ibrahim Abdullahi Gusau, ya ce: “Abin da ya faru a makwabciyarmu jiyar Katsina ya tilasta mana rufe wadannan makarantu duk da cewa saura mako guda zangon karatun da ake ciki zai kare”.

Ya ce daukar matakin ya zama dole don a dakile rashin doka da oda a da kuma tabbatar da tsaron dalibai; duk da cewa za a ci gaba da sha’anin koyo da koyarwa a sauran makarantu.

“Makarantun da [umarnin] ya shafa na wurare ne da ke kan iyakar jiharmu da makwabtanmu, Katsina da Kaduna”, inji shi.

Makarantun da aka rufen su ne:

  1. G.S.S. Tsafe (Raka boarding)
  2. G.S.S Birnin Magaji (Boarding)
  3. G.D.S.S. Nasarawa Mailayi (je-ka, ka-dawo)
  4. G.D.S.S. Gusami (je-ka, ka-dawo)
  5. G.A.S.S. Zurmi (ta kwana)
  6. G.D.S.S. Gurbin Bore (Je-ka, ka dawo)
  7. G.G.S.S. Moriki (ta kwana)
  8. Science Secondary School, Shinkafi (ta kwana)
  9. Science Secondary School, Dansadau (ta kwana)
  10. Science Secondary School Bakkuyaum (ta kwana)

Sojoji sun kashe kwamandan ’yan bindiga da tarwatsa 300

Zaɓen 2027: Tinubu ya sake tsayar da Shettima mataimakinsa

Tinubu ya gaji yana buƙatar ya huta — Peter Obi

Ɗalibai da malamai da aka sace a Oyo sun kuɓuta