An sace ɗan shekara 79 a Kaduna

Maharan sun sace shi ne a daren ranar Juma’a.

An sace ɗan shekara 79 a Kaduna

An yi garkuwa da wani mutum mai shekara 79 a duniya, Kwamared Elder Takai Agang Shamang a gidansa da ke Bikini-Tsourarang, Manchock a ƙaramar hukumar Kaura ta Jihar Kaduna.

Aminiya ta ruwaito cewar an sace shi ne da misalin ƙarfe 7:30 zuwa ƙarfe 8 na daren ranar Juma’a.

Misis Grace Yohannah Abbin, wadda ’ya ce ga mutumin, ta tabbatar da faruwar lamarin da safiyar Lahadi.

A cewarta, wasu gungun mahara sun kutsa cikin gidan mahaifinta da ƙarfi kuma suka tafi da shi.

Kwamared Shamang, ya yi fice wajen gudanar da ayyukan jin-ƙai da ƙungiyar ƙwadago kuma mutum ne wanda ake girmamawa a yankin.

Ta ce hukumomi a Jihar Kaduna na gudanar da bincike kan lamarin.

“Al’umma da ’yan uwa suna kira ga jama’a su taimaka da duk wani bayani da zai taimaka wajen dawowarsa lafiya,” in ji ta.

Kakakin rundunar ’yan sandan Kaduna,  Mansir Hassan, bai ce komai game da faruwar lamarin ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

’Yan sanda sun ƙwace sakamakon zaɓe a Ribas

Yadda mutanen Jigawa suka ƙi fita zaɓen ƙananan hukumomi 

Za mu yi wa Kwankwaso ritaya a 2027 — Doguwa

’Yan daba sun ƙone ofishin hukumar zaɓen Akwa Ibom