An sace jami’in gwamnati a kusa da sansanin sojin Abuja
’Yan bindiga sun kai hari a kusa da sansanin sojojoi a Abuja, inda suka dauke wani darakta a hukumar samar da gidaje ta kasa.
![An sace jami’in gwamnati a kusa da sansanin sojin Abuja An sace jami’in gwamnati a kusa da sansanin sojin Abuja](https://aminiya.ng/wp-content/uploads/2023/08/Abuja-city.jpg)
ƙofar shiga birnin tarayya Abuja
’Yan bindiga sun kai hari a kusa da sansanin sojojoi a Abuja, inda suka dauke wani darakta a hukumar samar da gidaje ta kasa.
Maharan sun kai harin ne a yankin Karamar Hukuamr Bwari inda suka dauke Mista Aondo Ver.
Cikin mutanen da ke zaune a yankin da al’amarin ya faru, akwai jami’an tsaro da ke aiki, da wadanda suka yi ritaya da dama.
A kwanakin nan Abuja na fama da matsalar tsaro, abun da ya sa ake ta kira ga mahukunta dasu gaggauta daukar matakan magance matsalar.