An sace magidanci a hanyar kai dansa jarabawar JAMB
Magidanci an sace shi yayin da ya ke kan hanyar kai dansa zana jarabawar Jamb.
Mahara
Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace wani magidanci a yayin da yake kai dansa zana jarabawar JAMB domin neman gurbin shiga manyan makarantu a Jihar Edo.
Bayanai sun nuna lamarin ya faru sa misalin karfe 7 na safiyar ranar Asabar a kan babban titin Benin zuwa Legas a Karamar Hukumar Ovia ta Arewa Maso Gabas, a Jihar Edo.
- Wani mutum ya kamu da cutar Kyandar Biri a Landan bayan ya ziyarci Najeriya
- 2023: Matsalar tsaro da ilimi zan fi bai wa muhimmanci —Amaechi
Rahotanni sun ce magidancin ya dauki dansa zai kai shi cibiyar zana jarabawar ta JAMB ne a kan babur din haya, daga bisani maharan suka yi awon gaba da shi.
An gano cewa bayan maharan sun sace magidancin shi kadai, sai suka bar dan a inda abin ya faru.
Kakakin ’yan sandan Jihar Edo, Bello Kontongs, ya tabbatar mana cewa maharan sun sace mutumin ne a lokacin da yake kai dansa inda zai zana jarabawar ta JAMB.
Sai dai ya ce tuni aka baza ’yan sanda a dajin don ceto magidancin daga hannun maharan ba tare da wani abu ya same shi ba.