An sanya dokar hana fita a ƙananan hukumomi 3 a Yobe

Gwamna Buni ya yaba wa matasan da suka janye daga shiga zanga-zangar matsin rayuwa a jihar.

An sanya dokar hana fita a ƙananan hukumomi 3 a Yobe

Jihar Yobe

Gwamnatin Yobe ta sanar da sanya dokar hana fita ta sa’o’i 24 a ƙananan hukumomi uku na jihar.

Ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Potiskum, Nguru, da kuma Gashua.

Hakan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mashawarcin gwamnan jihar na musamman kan harkokin tsaron, Birgediya-Janar Dahiru Abdulsalam mai ritaya ya fitar a yau Alhamis.

Sanarwar ta ce ɗaukar matakin ya zama tilas la’akari da yadda wasu ɓata-gari ke fakewa da zanga-zangar matsin rayuwa suna sacewa da lalata kadarorin jama’a da na gwamnati.

Abdulsalam ya ce a yayin da ake umartar jami’an tsaro da su tabbatar an kiyaye dokar, yana kuma shawartar jama’ar ƙananan hukumomin da su zauna a gida domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro.

Kazalika, Gwamna Mai Mala Buni ya yaba wa al’ummar jihar musamman matasan da suka amsa kiran janyewa daga zanga-zangar matsin rayuwa la’akari da ƙalubalen tsaro da ake fuskanta a jihar.

Ban zama Shugaban Kasa don na tara kuɗi ba — Tinubu

Babu buƙatar mu riƙa tsayar da motoci muna duba takardu — ’Yan sanda

‘Yan bindiga sun ƙone gidan mai da motoci 4 a Enugu

Kwalara ta kashe fiye da mutum 300 a Sudan