An sanya dokar hana fita a Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita ta daga safe zuwa dare na tsawon sa’a 24 a cikin garin Kaduna da kewaye sakamakon rikicin  da ya haddasa rasuwa da raunata wasu jama’a da dama a yankunan. Majiyarmu ta bankado cewa, tun lokacin da aka sace sarkin Adara, Agom Adara, Mista Maiwada Galadima, aka fara […]

An sanya dokar hana fita a Kaduna

Nasir El-Rufai, Gwamnan Jihar Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanya dokar hana fita ta daga safe zuwa dare na tsawon sa’a 24 a cikin garin Kaduna da kewaye sakamakon rikicin  da ya haddasa rasuwa da raunata wasu jama’a da dama a yankunan.

Majiyarmu ta bankado cewa, tun lokacin da aka sace sarkin Adara, Agom Adara, Mista Maiwada Galadima, aka fara samun rahotanni tashin hankali wanda ya fara daga Kasuwar Magani inda aka kashe akalla mutum 55 a cikin kwana uku da suka gaba ta.