An sauya Kwamishinan ’Yan Sandan Kano

CP Ussaini Mohammed Gumel ya mika ragamar jagoranci ga sabon Kwamishinan ’Yan Sandan da ka tura Jihar Kano, Salman Dogo Garba

An sauya Kwamishinan ’Yan Sandan Kano

Hedikwatar ‘yan sandan Jihar Kano

Salman Dogo Garba ya karbi ragamar aiki a matsayin sabon Kwamishinan ’Yan Sandan Kano.

A ranar Litinin din nan CP Salman Dogo ya karbi jagorancin rundunar daga Hussaini Mohammed Gumel, wanda ya sami karin girma.