An sauya ranar zaɓen ƙananan hukumomin Kano

Jam’iyyu za su fara yaƙin neman zaɓe daga 1 ga watan Satumba sannan a kammala a ranar 25 ga Oktoba.

An sauya ranar zaɓen ƙananan hukumomin Kano

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf

Hukumar Zaɓe ta Kano (KANSIEC) ta yi wani ƙwarya-ƙwaryar gyara game da ranar da za a gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi a jihar.

Shugaban Hukumar, Faresa Sani Lawan Malumfashi ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai a Kano.

Farfesa Malumfashi ya ce sakamakon wannan canji da aka samu a yanzu za a gudanar da zaɓen ne a ranar 26 ga Oktoba, a maimakon 30 ga Nuwamba da aka sanya da farko.

A cewarsa, an yanke shawarar janyo kwanakin zaɓen ne domin yi wa Kotun Ƙoli biyayya wadda bayan nan ta bai wa ƙananan hukumomin ’yancin gashin kansu.

Ya ƙara da cewa, jam’iyyu za su fara yaƙin neman zaɓe daga 1 ga watan Satumba sannan a kammala a ranar 25 ga Oktoba.

Kashim Shettima zai jagoranci tawagar Nijeriya a taron MDD

NECO ta fitar da sakamakon jarrabawar 2024

Kano: Abba ya rusa ciyamomin riko

An haramta wa ma’aikatan Asibitin Tarayya yin ‘kirifto’ a wurin aiki