An tsinci gawar ma’aikacin gwamnati wata daya bayan sace shi

An samu gawar ma’aikacin a wani rami, wata daya bayan sace shi.

An tsinci gawar ma’aikacin gwamnati wata daya bayan sace shi

’Yan sanda a lokacin da suke bude ramin da wasu wadanda ake zargi suka jefa gawar matar da suka kashe. (Tsohon hoto).

An tsinci gawar ma’aikacin Karamar Hukumar Katsina-Ala da ke Jihar Binuwai, a wani rami wata daya bayan an sace shi.

An gano gawar mutumin ne a wani rami a Akpera da ke yankin Tongov, a karamar hukumar.

Rahotanni sun ce an sace mutumin ne wata daya da ya wuce, kuma iyalansa sun kasa gano inda yake.

Bayan gano gawar tasa, dan majalisar yankin da jami’an tsaro sun tona gawar tasa da aka binne.

Bayan tono gawar Myaan, an kai ta dakin ajiye gawarwaki na Babban Asibitin Katsina-Ala.

Da yake jawabi ga menama labarai, Shugaban Karamar Hukumar, Alfred Atera, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Yayin da wakilinmu ya yi kokarin ganawa da kakakin ’yan sandan jihar, DSP Catherine Anene, abun ya ci tura.

‘Na yi wa maigidana yankan rago don kar na biya shi bashi’

NAJERIYA A YAU: Alkiblar Da Edo Za Ta Fuskanta Bayan Zaben Monday Okpebholo

Bidiyon Tsiraici: Hafsat Baby ta shiga hannun Hisbah

Okpebholo ya lashe zaɓen Gwamnan Edo