An yi artabu tsakanin jami’an tsaro da masu zanga-zangar Iraki

Masu zanga-zanga a Iraki sun kara arangama da jami’an ‘yan sanda a binrin Baghdad, a daidai lokacin da suke cika shekara daya da zanga-zangar kin jinin gwamnati mai ci. A ranar Litinin ’yan sanda suka tarwata dubban masu zanga-zangar ta hanyar harba musu hayaki mai sa hawaye. #EndSARS: Farashin shinkafa ’yar waje ya fadi warwas ’Yan […]

An yi artabu tsakanin jami’an tsaro da masu zanga-zangar Iraki
Masu zanga-zanga a Iraki sun kara arangama da jamian yan sanda a binrin Baghdad, a daidai lokacin da suke cika shekara daya da zanga-zangar kin jinin gwamnati mai ci.

A ranar Litinin ’yan sanda suka tarwata dubban masu zanga-zangar ta hanyar harba musu hayaki mai sa hawaye.

Bangarorin sun yi dauki ba dadi ne s daidai lokacin da masu zanga-zangar ke kona tayoyi da jefe-jefe a kan gadar Al-Jumhuriyah, da ake bi a tsallake kogin Tigris, zuwa yankin Green Zone.

Hanyar Green Zone na cike da matakan tsaro, kuma wuri ne mai ofisoshin jami’an gwamnati, da na jakadacin Amurka.

Idan ba a manta ba, masu zanga-zangar da suka gudanar a bara, sun mamaye manyan garuruwa da ke Kudanci Iraki inda mabiya akidar Shi’a ke da rinjaye.

Za a yi jana’izar jagoran addinin Iran Ali Khamenei a watan Yuli

Fiye da ƙungiyoyi 60 sun yi zanga-zanga kan taron G7 a Faransa

Boko Haram sun ƙone makarantu a Borno

Har yanzu ’yan bindiga ba su saki matar Manjo Janar Rabe ba